Yadda za ta kaya a gasar cin kofin Afirka na 2024

Asalin hoton, Getty images

Ivory Coast mai masaukin baƙi za ta fafata da Najeriya a matakin rukuni a gasar cin kofin nahiyar Afirka inda aka hada su a rukunin A.

Ƙasar wanda ta lashe gasar a 1992 da 2015 za ta buɗe gasar ne a ranar 13 ga watan Janairu inda za ta kara da Guinea-Bissau, yayin da Equatorial Guinea za ta kasance ƙungiya ta hudu a rukunin.

Senegal mai rike da kofin Afirka za ta fafata da Kamaru a matakin rukuni na gasar, zakarun na nahiyar Afirka sun fito ne a rukunin C, inda za su kara da makwabtansu Gambia da kuma Guinea.

Ƙasar da ta kai wasan kusa da na ƙarshe a gasar cin kofin duniya da kuma mai masaukin baƙi a shekarar 2025 Morocco za ta kara da DR Congo a matakin rukunin F, Zambia da kuma Tanzania.

Crédit: Lien source

Les commentaires sont fermés.